fidelitybank

Majalisa ta yi gyara a kan dokar hana biyan kudin fansa ga msu garkuwa da mutane

Date:

Majalisar dattawa ta yi gyara ga dokar ta’addanci, 2013, inda ta haramta biyan kudin fansa ga masu garkuwa da mutane a Najeriya.

Ƙaddamar da Dokar Ta’addanci na 2013, ya biyo bayan nazarin rahoton kwamitin majalisar dattijai kan harkokin shari’a, ‘yancin ɗan adam da shari’a.

Shugaban kwamitin, Sanata Opeyemi Bamidele (APC, Ekiti ta tsakiya) ne ya gabatar da rahoton kafin a duba.

Bamidele, a cikin jawabinsa, ya ce kudirin dokar ya tanadi haramta biyan kudin fansa ga masu garkuwa da mutane da kuma ‘yan ta’adda, domin a sako duk wani wanda aka tsare ba bisa ka’ida ba, daure ko kuma sace shi.

A cewar dan majalisar, “Babban abin da aka shigo da wannan kudiri shi ne don dakile karuwar satar mutane da sace-sacen kudin fansa a Najeriya, wanda ke yaduwa a fadin kasar.”

Ya bayyana cewa, a cikin takardar da aka gabatar wa kwamitin, an tabo batutuwan da suka shafi batun ta’addanci da kuma bayar da kudaden ta’addanci daidai da kyawawan ayyuka na duniya.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp