fidelitybank

Majalisa ta yi binciken ɓatan bindigogin mu cikin sirri – Ƴansanda

Date:

Sifeto Janar na ƴansanda Najeriya, Kayode Egbetokun ya rubuta wa majalisar dattawa wasiƙa yana roƙonta cewa binciken da za a ci gaba da yi dangane da ɓatan bindigogi 3,907 ya kasance a sirrance bisa dalilan tsaro.

Sai a wasiƙar, sifeto janar na ƴansandan ya yi watsi da rahoton 2019 da ofishin babban mai bincike da gwamnatin tarayya ya fitar wanda ya yi ikrarin ba a san inda dubban bindigogin ƴansanda suka shiga ba ya zuwa watan Janairun 2020 inda ya bayyana rahoton da cewa cike yake da kurakurai.

Wasiƙar wadda aka karanta ta a majalisar dattawa bayan amince wa da kasafin kuɗin ƙasar na 2025 a ranar Alhamis, na zuwa ne sa’a 48 bayan wani zaman saurare da kwamitin majalisar dattawa mai binciken kashe-kashen kuɗaɗen gwamnati inda rundunar ƴansandan ta yi ta nuƙu-nuƙu wajen kare kanta.

Sifeto Janar na ƴansandan, kayode Egbetokun wanda ya kasance a wurin sauraron bahasin ranar Talata kafin daga bisani ya nemi uzuri ya bar zaman, ya soki yadda ake neman titsiye rundunar ƴansandan ƙasar a bainar jama’a.

Ya ƙara da cewa bai dace a rinƙa tattuna irin waɗannan batutuwan a bainar jama’a ba.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp