fidelitybank

Majalisa ta titsiye shugaban kungiyar Malamai ta ASUU

Date:

Wasu mambobin majalisar wakilai, sun titseye shugaban ƙungiyar malaman jami’o’in ƙasar ASUU Farfesa Emmanuel Osodeke, kan wasu zarge-zarge da ya yi na cewa kakakin majalisar Femi Gbajabiamila ya yaudari ƙungiyar wajen jan hankalinta domin janyewa daga yajin aikin da ta shafe watanni tana yi.

Jaridar Daily Trust  ta ruwaito cewa, a wata hira da shugaban ASUU ya yi da wata jarida a ranar talata ya zargi Gbajabiamila da cewa, ya yi amfani da yaudara wajen sanya ƙungiyar janye yajin aikin da ta shafe wata takwas ta na gudanarwa a watan Oktoba.

Ta hanyar rubutaccen alƙawarin cewa, gwamnatin tarayya za ta biya malaman duka albashin watannin da ta riƙe musu ba tare da ɓata lokaci ba.

Yayin da yake mayar da martani game da zargin na shugaban ASUU a Abuja, mai magana da yawun majalisar wakilan ƙasar Benjamin Okezie Kalu ya ce babu inda kakakin majalisar ya yi alƙawarin warware matsalar albashin da malaman ke bin gwamnatin tarayya bashi.

Inda ya ce, majalisar wakilan ta taimaka ne kawai wajen kawo ƙarshen yajin aikin, ta hanyar yin ƙoƙari wajen inganta albashin malaman jami’o’in tare da taimakawa wajen samar da kuɗin inganta jami’o’in ƙasar.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp