‘Yan Majalisar Dattawa, sun tilasta wa Dr. Bosun Tijani neman afuwarsu da kuma ‘yan Najeriya game da wasu kalamai da ya yi a shafukan zumunta a baya.
Dr. Tijani na cikin mutanen da Shugaba Bola Tinubu ya aika wa Majalisar don tantance su a matsayin ministocin gwamnatinsa, wanda ɗan jihar Ogun ne.
Sanatocin sun karanto irin saƙonnin da ya wallafa a Twitter, cikinsu har da na 2019, inda ya ce “ba na alfahari da riƙe fasfo ɗin Najeriya da kuma Najeriya a matsayinta na ƙasa”.
Haka nan, an karanto wani saƙon da ya kira ‘yan Majalisar “shashashai” game da yadda suke tantance ministoci.
Mista Tijani bai musanta zarge-zargen ba.
Bayan sanatoci da dama sun yi magana, masu goyon bayansa da masu neman ƙarin bayani, Shugaban Majalisa Godswill Akpabio ya umarce shi da ya nemi afuwarsu kafin su ƙyale shi ya tafi.
“Ina neman afuwarku ‘yan Majalisa da ma sauran Najeriya kan waɗannan abubuwan da na faɗa,” in ji shi. “Ina so ku lura da dalilan da suka sa na yi su, ban yi su don na ɓata sunan wani ba.”
Daga nan ya rusuna kuma ya sauka daga kan dandamali.