fidelitybank

Majalisa ta tirsasa Bosun ya baiwa ‘yan Najeriya hakuri bayan tantance shi

Date:

‘Yan Majalisar Dattawa, sun tilasta wa Dr. Bosun Tijani neman afuwarsu da kuma ‘yan Najeriya game da wasu kalamai da ya yi a shafukan zumunta a baya.

Dr. Tijani na cikin mutanen da Shugaba Bola Tinubu ya aika wa Majalisar don tantance su a matsayin ministocin gwamnatinsa, wanda ɗan jihar Ogun ne.

Sanatocin sun karanto irin saƙonnin da ya wallafa a Twitter, cikinsu har da na 2019, inda ya ce “ba na alfahari da riƙe fasfo ɗin Najeriya da kuma Najeriya a matsayinta na ƙasa”.

Haka nan, an karanto wani saƙon da ya kira ‘yan Majalisar “shashashai” game da yadda suke tantance ministoci.

Mista Tijani bai musanta zarge-zargen ba.

Bayan sanatoci da dama sun yi magana, masu goyon bayansa da masu neman ƙarin bayani, Shugaban Majalisa Godswill Akpabio ya umarce shi da ya nemi afuwarsu kafin su ƙyale shi ya tafi.

“Ina neman afuwarku ‘yan Majalisa da ma sauran Najeriya kan waɗannan abubuwan da na faɗa,” in ji shi. “Ina so ku lura da dalilan da suka sa na yi su, ban yi su don na ɓata sunan wani ba.”

Daga nan ya rusuna kuma ya sauka daga kan dandamali.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp