fidelitybank

Majalisa ta Tara ta karɓi ƙorafi 705 cikin shekaru 4 – Lawal

Date:

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya mai barin gado, Ahmad Ibrahim Lawan, ya ce Majalisa ta Tara da ya jagoranta ta karɓi ƙorafi 705 daga ɗiɗaikun ‘yan ƙasar cikin shekara huɗu.

Da yake jawabin bankwana a ranar Asabar a zauren Majalisar, Ahmad Lawan ya ce sun samu ƙorafi 146 a shekarar farko, 239 a shekara ta biyu, 232 a shekara ta uku, da kuma 88 a ta uku.

“Dukkansu suna matakai daban-daban na samun biyan buƙata,” in ji shi.

Kazalika, ‘yan Majalisa ta Tara sun gabatar da ƙudiri 361 (motion) sannan kuma suka ɗauki matsaya (resolution) 488 a kan batutuwa daban-daban da suka ja hankalin gwamnati a kansu, a cewarsa.

“Kwamatocin sa-ido na Majalisa ta Tara sun kai ziyarar aiki 371 zuwa ma’aikatu da sashe-sashe da hukumomi da kuma wuraren gudanar da ayyuka a faɗin ƙasa,” kamar yadda ya bayyana.

A ranar Talata mai zuwa ake sa ran za a rantsar da Majalisa ta 10, yayin da ake ci gaba da tafka siyasa game da wanda zai maye gurbin Ahmad Lawan a matsayin shugaba.

Jam’iyyar APC mai mulki dai na son ‘yan majalisar su zaɓi Godswill Akpabio daga Jihar Akwa Ibom a kudancin Najeriya, a matsayin shugaba, da kuma Barau Jibrin daga Kano a arewacin ƙasar a matsayin mataimakinsa.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp