Majalisar Dattawa ta tantance ƙarin mutum uku daga cikin waɗanda Shugaba Tinubu ya nemi amincewarta don naɗa su ministoci.
Mutanen da aka tantance sun haɗa da Sanata Ibrahim Geidam, tsohon Gwamnan Yobe, da Sanata Aliyu Sabi Abdullahi daga jihar Neja da kuma Sanata Heineken Lokpobori daga jihar Bayelsa.
Majalisar ta nemi su yi gaisuwa ne kawai su fita bayan sun gabatar da taƙaitaccen tarihinsu, kasancewar sun taɓa zama ƴan majalisa kuma kundin aikin Majalisar Dattawa ya amince da hakan.
Suna cikin ƙarin mutum 19 da Tinubu ya aika wa Majalisar ranar Laraba.