Majalisar Dattawa ta tabbatar da Ola Olukoyede a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da cin hanci da rashawa (EFCC).
Hakazalika majalisar ta tabbatar da nadin Muhammad Hammajoda a matsayin sakataren hukumar.
Tabbatar da mutanen biyu ya biyo bayan tantance su ne da babban zauren majalisar ya yi a yau ranar Laraba kimanin mako guda bayan da shugaba Bola Tinubu ya nada su.


