fidelitybank

Majalisa ta tabbatar da Lauretta a matsayin shugabar hukumar yankin Neja Delta

Date:

Duk da sukar da ake yi mata, majalisar dattawa a ranar Talata, ta tabbatar da nadin mataimakiyar shugaban kasa ta musamman kan sabbin kafafen yada labarai, Lauretta Ifeanyi-Onochie a matsayin babbar shugabar hukumar raya yankin Neja Delta.

Majalisar dattijai a zauren majalisar ta kuma tabbatar da wasu mutane 12 biyo bayan tantance wadanda aka nada a ranar Juma’ar da ta gabata a harabar majalisar dokokin kasar.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci majalisar dattijai ta tabbatar da nadin mataimakiyarsa ta musamman kan sabbin kafafen yada labarai, Lauretta Ifeanyi-Onochie a matsayin babbar shugabar hukumar raya yankin Neja Delta, lamarin da ya janyo yabo da tofin Allah tsine a wasu bangarori.

Buhari ya kuma bayyana sunayen wasu mutane 14 a cikin wasikar a matsayin Manajan Darakta, Daraktoci da membobin hukumar.

Sun hada da Samuel Ogokwu, daga Jihar Bayelsa, a matsayin Manajan Darakta, wanda zai yi wa’adin shekaru biyu don kammala wa’adin mulkin da ya gabace shi.

Haka kuma jerin sunayen sun hada da Dimgba Erugba, mai wakiltar jihar Abia, Dr. Emem Willcox Wills (Akwa Ibom), Dattijo Denyanbofa Dimaro (jihar Bayelsa), Hon. Orok Duke (Cross River) da Dr. Pius Odudu (Jihar Edo).

Injiniya Anthony Ekenne, (Jihar Imo), Hon. Gbenga Edema (Jihar Ondo), Elekwachi Dimkpa (Jihar Rivers), Alhaji Mohammed Kabir Abubakar, (Jihar Nasarawa, mai wakiltar shiyyar Arewa ta tsakiya), Alhaji Sadiq Sami Sule – Ikoh (jihar Kebbi, Arewa-maso-Yamma) da kuma Farfesa Tahir Mamman SAN. , (Jhar Adamawa, Arewa maso Gabas)
Shugaban ya kuma zabi Manjo-Janar Charles Airhiavbere (rtd) daga jihar Edo a matsayin (Babban Darakta, Kudi) da Charles Ogunmola, daga jihar Ondo, a matsayin Babban Daraktan, Projects shi ma ya sanya jerin sunayen wadanda aka nada a NDDC.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp