fidelitybank

Majalisa ta tabbatar da Lauretta a matsayin shugabar hukumar yankin Neja Delta

Date:

Duk da sukar da ake yi mata, majalisar dattawa a ranar Talata, ta tabbatar da nadin mataimakiyar shugaban kasa ta musamman kan sabbin kafafen yada labarai, Lauretta Ifeanyi-Onochie a matsayin babbar shugabar hukumar raya yankin Neja Delta.

Majalisar dattijai a zauren majalisar ta kuma tabbatar da wasu mutane 12 biyo bayan tantance wadanda aka nada a ranar Juma’ar da ta gabata a harabar majalisar dokokin kasar.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci majalisar dattijai ta tabbatar da nadin mataimakiyarsa ta musamman kan sabbin kafafen yada labarai, Lauretta Ifeanyi-Onochie a matsayin babbar shugabar hukumar raya yankin Neja Delta, lamarin da ya janyo yabo da tofin Allah tsine a wasu bangarori.

Buhari ya kuma bayyana sunayen wasu mutane 14 a cikin wasikar a matsayin Manajan Darakta, Daraktoci da membobin hukumar.

Sun hada da Samuel Ogokwu, daga Jihar Bayelsa, a matsayin Manajan Darakta, wanda zai yi wa’adin shekaru biyu don kammala wa’adin mulkin da ya gabace shi.

Haka kuma jerin sunayen sun hada da Dimgba Erugba, mai wakiltar jihar Abia, Dr. Emem Willcox Wills (Akwa Ibom), Dattijo Denyanbofa Dimaro (jihar Bayelsa), Hon. Orok Duke (Cross River) da Dr. Pius Odudu (Jihar Edo).

Injiniya Anthony Ekenne, (Jihar Imo), Hon. Gbenga Edema (Jihar Ondo), Elekwachi Dimkpa (Jihar Rivers), Alhaji Mohammed Kabir Abubakar, (Jihar Nasarawa, mai wakiltar shiyyar Arewa ta tsakiya), Alhaji Sadiq Sami Sule – Ikoh (jihar Kebbi, Arewa-maso-Yamma) da kuma Farfesa Tahir Mamman SAN. , (Jhar Adamawa, Arewa maso Gabas)
Shugaban ya kuma zabi Manjo-Janar Charles Airhiavbere (rtd) daga jihar Edo a matsayin (Babban Darakta, Kudi) da Charles Ogunmola, daga jihar Ondo, a matsayin Babban Daraktan, Projects shi ma ya sanya jerin sunayen wadanda aka nada a NDDC.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp