Majalisar dattawa ta amince da naɗin Laftana Janar Olufemi Oluyede a matsayin babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya.
Amincewar da majalisar ta yi yau ta biyo bayan nazarin rahoton kwamitinta mai kula da harkokin rundunar sojin ƙasa, wanda Sanata Abdulaziz Musa Yar’ adua ke shugabanta.
Majalisar ta amince da murya ɗaya shawarwarin da kwamitin ya bayar a rahoton.
Shugaba Tinubu ne ya naɗa Laftana Janar Oluyede, a matsayin mai riƙon muƙamin shugaban rundunar sojojin ƙasa sakamakon rashin lafiya da kuma rasuwar mai muƙamin, Laftana Janar Taoreed Abiodun Lagbaja,.