fidelitybank

Majalisa ta soki jihohi kan rashin kyakkyawan shirin aikin hajji

Date:

Majalisar dattijawa ta soki lamirin wasu jihohin ƙasar nan kan yadda suka gaza yin shiri mai kyawu a aikin hajjin da ke gudana yanzu haka a ƙasar Saudiyya.

Ko a shekarun da suka gabata mahajjata sun sha kokawa kan matsalar masauki da na abinci, lamarin da ya rataya a wuyan hukumomin kula da mahajjata na jihohi.

A tattaunawarsa da BBC, shugaban kwamitin kula da aikin hajji na Majalisar Dattijan Najeriya, Ali Ndume, ya ce sun damu matuƙa game da rashin kyakkywan makwancin mahajjata a filin Mina, inda aka samu cunkoso mai yawa.

Ya ce: “Babbar matsalar da aka samu ta faru ne a filayen Mina da Arafat da kuma wajen jifa”.

Ya ƙara da cewa “lamarin ya jefa mutane cikin mawuyacin hali, sansanin da aka ba su akwai matsi, ya yi cunkoso ƙwarai da gaske”.

“Katifar da aka bai wa mahajjata ƙarama ce sosai kuma an harhaɗa su a matse…Inda wata cuta ta ɓarke da za a iya samun matsaloli sosai”.

Wannan na zuwa ne yayin da mahajjata a ƙasar ta Saudiyya suka koka kan zafin yanayi.

Lamarin da ya yi sanadiyyar mace-macen maniyyata da dama.

Ƙasar Jordan ta bayyana cewa alhazanta guda 14 ne tsananin zafi ya yi sanadiyyar rasuwarsu a ƙasar ta Saudiyya sa’ilin aikin hajjin na wannan shekara.

A ɓangare guda, sanata Ali Ndume ya nuna damuwa kan yadda aka ajiye mahajjata a wuri mai nisa a Mina da kuma wajen jifan sheɗan.

Ya ƙara da cewa hakan na nuna cewa an samu tangarɗa wajen shirye-shiryen aikin hajjin bana.

Ya kuma alaƙanta waɗannan matsaloli ga jihohi, musamman na arewacin Najeriya waɗanda ke da mahajjata masu yawa, waɗanda ya ce ba su yi shirin da ya kamata ba.

Sanata Ndume ya ce bayan kammala aikin hajjinna bana, kwamitinsa zai tattauna da hukumar alhazai ta Najeriya da kuma na jihohi domin ganin an hana faruwar irin haka a gaba.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp