fidelitybank

Majalisa ta kaddamar da bincike a kan guduwar jami’in Binance a Najeriya

Date:

Majalisar wakilai ta kaddamar da bincike kan yadda Nadeem Anjarwalla, Shugaban Binance na yankin Africa ya kubuta daga hannun mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro.

Kudurin ya biyo bayan kudirin da Dennis Okafor ya gabatar da shi a ranar Laraba r nan yayin zaman majalisar.

Idan dai za a iya tunawa, an tsare Mista Anjarwalla da Tigran Gambaryan a Abuja kafin ya tsere daga gidan ajiya da gyaran hali, daga bisani kuma ya fice daga kasar nan.

A cikin kudirin, Okafor ya ce, tserewar Anjarwalla daga gidan yari abin kunya ne ga Najeriya.

Ya kuma roki majalisar da ta binciki lamarin da ya kai ga ya cika wndon sa da iska.

A halin da ake ciki, majalisar ta kuma musanta zargin neman cin hancin da rashawa daga hannun wasu mutane da aka yi ikirari.

Shi kuwa Kama Nkem Kanma, ya yi tsokaci kan batun, inda ya bayyana cewa majalisar ba za ta iya jure wannan abun kunyar ba.

Ko da yake dan majalisar bai ambaci kamfanin Binance ba, duk da a baya ne dai shugaban kamfanin na Binance Richard Teng ya zargi wasu ‘yan majalisar da neman cin hanci daga hannunsu.

Teng, a cikin wani sako da ya wallafa a shafin X ranar Talata, ya zargi kwamitin majalisar wakilai kan laifukan kudi da neman nagoro daga hannun kamfanin na Binance.

Kanma ya ce majalisar ba ta taba yin irin wannan bukata daga Binance ba kuma ta yi kira da a dauki kwakkwaran mataki.

Da yake yanke hukunci kan batun, kakakin majalisar Tajudeen Abbas ya umarci magatakardar majalisar, Yahaya Danzaria da ya yi amfani da kafafen yada labarai wajen karyata ikirarin.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp