fidelitybank

Majalisa ta gayyaci shugaban Kwastom

Date:

Kwamitin Majalisar Wakilai kan karɓar ƙorafe-ƙorafen jama’a, ya gayyaci babban kwanturolun hukumar kwastom, Adewale Adeniyi, domin ya yi mata bayani kan abin da ya sa wasu manyan jami’an hukumar suka ƙi yin ritaya duk kuwa da lokacinsu ya yi.

Cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai na kwamitin, Chooks Oko ya fitar, ya ce an gayyaci babban jami’in hukumar ne domin ya yi bayani kan ƙorafin da aka shigar wa kwamitin dangane da ƙin yin ritaya da wasu manyan jami’an hukumar suka yi bayan lokacinsu na hakan ya yi.

Gidauniyar Obasi-Pherson Help ce ta shigar da ƙorafin gaban kwamitin , inda ta yi zargin cewa wasu jami’an hukumar masu muƙamin mataimakin kwanturola da masu muƙamin kwanturola sun ƙi ajiye aikinsu, bayan cikar lokacin.

Yayin bayar da sammacin, majalisar wakilan ta ce babban kwnturolan ƙasar ne kaɗai ke da haƙƙi bayyana wa ‘yan ƙasa ainihin gaskiyar wannan zargi.

“Ƴan Najeriya sun cancanci sanin gaskiyar abin da ya faru daga bakin babban konturolan…, a wannan lokaci da mafi yawan matasanmu ke neman ayyukan yi, indai batun nan gaskiya ne, to babu adalci ace ga wasu tsofaffin da suka isa ritaya su ƙi yin hakan,” a cewar shugaban kwamitin, Mike Etaba.

Ya ƙara da cewa ”ba wai muna ɗaukar ɓangare ba ne, muna nazarin kowane batu ne bisa gaskiya domin tabbatar da adalci ga waɗanda suka cancance shi”.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp