fidelitybank

Majalisa ta gayyaci Ministan kuɗi a kan ɓatan kuɗaɗen man fetur

Date:

Kwamitin majalisar wakilai da ke bincike kan zargin ɓatan kuɗin man fetur, ya gayyaci ministar kudi, Zainab Shamsuna Ahmed, da Sakataren gwamnatin tarraya Boss Mustapha, da kuma ministan shari’a Abubakar Malami.

Yana neman su bayyana gabansa a wani ɓangare na binciken da yake yi.

Shugaban kwamitin, Mark Tersee Gbillah ne ya bayar da umarnin gayyatar jami’an gwamnatin, bayan kwamitin ya koma sauraron bahasi kan zargin ɓacewar kuɗin gangar man fetur miliyan 48 da aka sayar wa China da wasu masu kwarmata bayanai suka bayyana.

Karanta Wannan: Buhari ya kai ziyara masallacin Annabi S.A.W

Kwamitin na bincike ne kan zargin ɓatan sama da dala biliyan 2.4 na man fetur da aka fitar ba bisa ƙa’ida ba, domin sayar da shi, tun daga shekarar 2014 zuwa yau.

Mista Gbillah ya ce kwamitin ya ba da umarnin ne domin sanin irin rawar da – ma’aikatar kuɗi da sauran hukumomin gwamnati – suka taka musamman kan abin da ya shafi tsarin masu kwarmata bayanai.

”Mafi yawan matsalolin – abin da ya kamata mu bincika game da tsarin masu kwarmata bayanai – na tasowa ne tsakanin ma’aikatar kuɗi da ofishin ministan shari’a”.

Tun da farko kakakin Majalisar wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila wanda ya samu wakilcin Isiaka Ibrahim Ayokunle, ya nuna damuwa game da raguwar kuɗin shiga da ƙasar ke samu daga sayar da ɗanyen man fetur.

Ya ce abu ne mai tayar da hankali zargin da masu kwarmata bayanan suka yi cewa fiye da dala biliyan 2.4 na kuɗin gangar mai miliyan 48 ne suka ɓace a ƙasar.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp