Ƙungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya, ta buƙaci shugaban majalisar dattawan ƙasar, Godswill Akpabio da ya gaggauta janye dakatarwar da majalisar ta yi wa sanata Natasha Akpoti-Uduaghan saboda an yi hakan ne ba bisa ƙa’ida ba.
Haka kuma ƙungiyar ta SERAP ta ce dakatarwar da aka yi wa Natashan ba komai ba ne illa tauye mata ƴancinta na faɗin alabarkacin baki, wanda tsarin mulkin Najeriya ya bata.
A makon da ya gabata ne dai majalsair dattawan Najeriya ta sanar da dakatar da Sanata Natasha Uduagahn bayan kwamitin ladabtarwar majalsar ya zarge ta da karya wasu daga cikin dokokinta.