fidelitybank

Majalisa ta gaggauta bincikar hukumar Alhazai saboda ta gaza – Bago

Date:

Gwamnan jihar Neja Mohammed Umar Bago ya bayyana rashin gamsuwarsa kan yadda hukumar alhazan Najeriya Nahcon ta gudanar da shirye-shiryen aikin Hajji bana.

Yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Saudiyya game da yadda aka gudanar da aikin, Gwamna Bago ya yi kira ga majalisar dokokin ƙasar ta binciki Nahcon kan yadda ta kashe kuɗin tallafin aikin hajji na naira biliyan 90 da gwamnatin tarayya ta bai wa hukumar.

Gwamna Bago ya ce a matsayinsa na gwamna zai buƙaci ƙungiyar gwamnonin ƙasar ta yi kiran rusa hukumar Nahcon, saboda a cewarsa hukumar ba ta da wani amfani, ta gaza ta kowane fanni.

Ya ce ya kamata shirya aikin Hajji ya koma ƙarƙashin ikon jihohi ba gwamnatin tarayya ba.

”Gwamnatin tarayya ta girmi shirya aikin Hajji, wannan abu ne da ƙaramar hukuma za ta iya shiryawa, don haka ina kira a bar jihohi su riƙa shirya aikin Hajjin jihohinsu, kamar yadda wasu ƙasashen duniya ke yi”.

Gwamnan ya kuma nuna damuwarsa kan yadda ya ce Nahcon ta kasa samar wa gwamnoni da sauran manyan mutane masaukai a Minna.

”A ce kakakin majalisar wakilai na Najeriya da wasu gwamnoni sun kasa samun wurin da za su kwanta a filin Minna wannan abin takaici ne”.

”Wasu na cewa muna ƙorafin ne saboda abin ya shafe mu, haƙiƙa ya shafe mu saboda haka lokaci ya yi da za mu tashi mu yi kiran a mayar da shirya aikin Hajji ƙarƙashin jihohi”, in ji gwamnan.

Gwamnan ya kuma koka kan yadda ya ce mahajjata sun biya kuɗi masu yawa amma suka kasa samun wadataccen kuɗin guzuri daga Nahcon.

”Ta yaya mutum zai biya naira miliyan takwas amma ace dala 400 kawai za a ba shi? wannan abu ne da hankali ba zai ɗauka ba”.

Gwamna Bago ya kuma koka kan abinci da masaukai da hukumar Nahcon ta tanadar wa mahajjatan ƙasar.

Ya ƙara da cewa kamata ya yi hukumar Nahcon ta zama mai lura da ayyukan Hajji ba mai gudanar da shirye-shiryen aikin hajji ba.

Ya ce alhazan jihar Neja biyu ne suka rasu sakamakon rashin lafiya, yayin da huɗu suka mutu saboda tsananin zafi

Sai dai gwamnan ya ɗora alhakin mutuwar mutanen biyu – da suka rasu sakamakon rashin lafiya – kan hukumar Nahcon.

Ya ce inda hukumomin alhazan jihohi ne ke lura da lafiyar alhazan jihohin da an samu sauƙi wajen saurin gano cutar da alhazan ke ɗauke da ita da kuma magance ta makar yadda ya kamata.

”Amma babu wanda ya yi hakan, saboda Nahcon ce ke lura da ɓangaren lafiyar alhazai”

Gwamnan ya ce kamata ya yi hukumomin alhazai na jihohi su lura da alhazan jihohinsu.

”Ya kamata a bar jihohi su riƙa tantance alhazansu, su san irin lalurorin da alhazan ke ɗake da su, tare da irin magungunan da suke sha, domin sanin matakan da za su ɗauka na lura da waɗanna alhazan, amma babu wanda ya yi hakan , saboda Nahcon ce ke da alhakin gudanar da hakan” in ji shi.

Ba wannan ne karon farko da wani gwamna a Najeriya ya yi ƙorafi kan yadda hukumar Nahcon ta tafiyar da ayyukan Hajjin bana ba.

Ko a makon da ya gabata ma jaridun ƙasar sun ambato gwamnan jihar, Bauchi Sanata Bala Mohammed na ƙorafin yadda hukumar Nahcon ta tafiyar da shirye-shiryen aikin Hajjin na bana.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp