fidelitybank

Majalisa ta gabatar da kudiri don magance matsaloli a kan kasafin kudi

Date:

Majalisar wakilai ta gabatar da wasu kudirori guda biyu domin magance matsalolin da ake samu kan jinkirin gabatar da kasafin kudin da shugaban kasa da gwamnoni ke yi tare da takaita adadin karin kasafin da za a amince da shi don magance gibin kudade a cikin kasafin shekara.

Kudirorin doka guda biyu suna gaban kwamitin wucin gadi kan sake duba akan kundin tsarin mulki na majalisar karkashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar, Benjamin Okezie Kalu.

Daya daga cikin kudurorin mai suna, “Kudirin dokar da za ta yi wa kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya kwaskwarima, 1999 domin takaita wa’adin gabatar da kasafin kudi a gaban majalisun dokoki na kasa da Jihohi.”

Kudirin ya samu ne ta hannun dan majalisa Mansur Manu Soro da kuma dan majalisar wakilai Emeka Martins Chinedu ya bukaci a bayyana lokacin da za a gabatar da kasafin kasa da na Jihohi a gaban Majalisar Kasa da Majalisun Jihohi don magance mummunan tasirin jinkirin da ake samu daga shugabanni wajen gabatar da kudurin.

Hakazalika, wani kudirin doka wanda dan majalisa Mansur Manu Soro da dan majalisa Adamu suka dauki nauyinsa ya nemi a takaita adadin karin kasafin kudi na kasa zuwa sau daya kawai a kowace shekara.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp