Majalisar Dattawa na bincike kan rahotonnin ɓacewar fiye da bindigogi 178,000, yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da addabar wasu yankunan ƙasar.
Haka kuma majalisar ta ce za ta gudanar da bincike kan rarraba kwangilar sayen makamai da ya kai na naira biliyan 1.1, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.
Cikin wani rahoton bincike da ofishin babban mai binciken kuɗi na ƙasar ya gabatar wa majalisar a 2019, ya ce ya gano yadda aka rarraba kwangilar sayen makaman.
Rahoton ya bayyana cewa “a watan Disamban 2018 akwai bindigodi 178,459 ciki har da ƙirar AK-47 88,078 da ba a san inda suke ba.
Haka ma zuwa watan Janairun 2020, aƙalla bindigogi da pistol 3,907 ne suka ɓata.
Ƴan majalisar dattawan sun ce suna fargabar bindigogin su faɗa hannun ɓata-gari, da ke ƙara dagula matsalar tsaro musamman a ƙasar da ke fama da rikicin Boko Haram da ƴanfashin daji da masu garkuwa da mutane.
Yayin da yake jawabi a madadin Babban Sifeton Ƴandan ƙasar, Mataimakan sifeton ƴansandan ƙasar, AIG Abdul Sulaiman ya ce wasu daga cikin bindigogin an sace su ne a lokacin fashi da hare-haren da ake kai wa ƴansanda.
Ya kuma buƙaci kwamitin majalisar dattawan ya ba shi ƙarin lokaci, domin gabatar da cikakken rahoto kan bindigogin da ba a san inda suken ba.