fidelitybank

Majalisa ta dukufa kan bacewar Bindigun ‘Yansanda dubu 178

Date:

Majalisar Dattawa na bincike kan rahotonnin ɓacewar fiye da bindigogi 178,000, yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da addabar wasu yankunan ƙasar.

Haka kuma majalisar ta ce za ta gudanar da bincike kan rarraba kwangilar sayen makamai da ya kai na naira biliyan 1.1, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Cikin wani rahoton bincike da ofishin babban mai binciken kuɗi na ƙasar ya gabatar wa majalisar a 2019, ya ce ya gano yadda aka rarraba kwangilar sayen makaman.

Rahoton ya bayyana cewa “a watan Disamban 2018 akwai bindigodi 178,459 ciki har da ƙirar AK-47 88,078 da ba a san inda suke ba.

Haka ma zuwa watan Janairun 2020, aƙalla bindigogi da pistol 3,907 ne suka ɓata.

Ƴan majalisar dattawan sun ce suna fargabar bindigogin su faɗa hannun ɓata-gari, da ke ƙara dagula matsalar tsaro musamman a ƙasar da ke fama da rikicin Boko Haram da ƴanfashin daji da masu garkuwa da mutane.

Yayin da yake jawabi a madadin Babban Sifeton Ƴandan ƙasar, Mataimakan sifeton ƴansandan ƙasar, AIG Abdul Sulaiman ya ce wasu daga cikin bindigogin an sace su ne a lokacin fashi da hare-haren da ake kai wa ƴansanda.

Ya kuma buƙaci kwamitin majalisar dattawan ya ba shi ƙarin lokaci, domin gabatar da cikakken rahoto kan bindigogin da ba a san inda suken ba.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp