Kwamitin ladabtarwa na majalisar Dattijawa ya dakatar da sanata Natasha Akpoti daga majalisar bisa zargin karya dokar majalisar ta hanyar bata sunan daya daga cikin yayan majalisar.
Wannan na zuwa ne bayan kusan mako biyu da aka kwashe ana zazzafar muhawara kan ruɗanin da ya shiga tsakanin sanatar da shugaban majalisar, Godswill Akpabio, lamarin da ya kai ga cewa Akpoti ta zargi shugaban majalisar da yunƙurin cin zarafinta ta hanyar lalata.
Sauran matakan da kwamitin ya bayar da shawarar É—auka a kan Natsha su ne:
– Majalisar ta janye ko rage tsawon lokacin dakatarwar idan sanatar ta nemi afuwar majalisa a rubuce.
Za a haramta mata shiga duk wasu hidimomin Majalisar daga ranar 6 ga watan Maris, 2025.
– A rufe ofishinta a tsawon lokacin sannan ta mika duk wasu kayan majalisar da ke hannunta
– A tsawon wata shida da za a dakatar da sanatar, za a haramta mata shiga harabar majalisar.
– A dakatar da albashinta da na ma’aikatanda ke taimaka mata na tsawon wata shida na dakatarwar da aka yi mata. Sai dai wasu sanatoci sun buÆ™aci a sassauta wannan matakin, inda daga baya majalisar ta amince cewar za a ci gaba da biyan hadimanta albashinsu a tsawon lokacin dakatarwar.
– Kada ta bayyana kanta a matsayin sanata a tsawon wata shida na lokacin dakatarwar.