fidelitybank

Majalisa ta bukaci Tinubu ya sa baki Isra’ila ta tsagaita wuta a Gaza

Date:

Majalisar dattijan Najerya ta buƙaci gwamnatin tarayya ta haɗa kai da wasu kasashe domin yin kira a tsagaita bude wuta a rikicin Isra’ila da Hamas.

Tun a ranar 7 ga watan Oktoba ne sojojin Isra’ila suke yin ruwan bama-bamai a Gaza, bayan mayaƙan Hamas sun ƙaddamar da harin da ya yi sanadin mutuwar mutum 1,400 a Isra’ila, waɗanda mafi yawansu fararen hula ne, a cewar hukumomin Isra’ila.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Hamas, adadin waɗanda suka mutu a Gaza ya zarce mutum 10,000 ciki har da yara sama da 4,000.

A wani kudiri da Sanata Abdulrahman Kawu daga Kano ta Kudu ya gabatar a ranar Talata, Majalisar Dattawar bayan muhawara mai zurfi ta bayyana mace-mace da kuma adadin waɗanda suka rasa muhallansu sakamakon rikicin na Isra’ila da Hamas a matsayin abin tsoro.

Yayin da suke bayyana ra’ayinsu, ƴan majalisar sun yi Allah-wadai da kashe-kashen da aka yi a bangarorin biyu, sannan suka buƙaci a zauna lafiya domin kauce wa abin da zai kawwo yaɗuwar rikicin.

Wannan kiran na zuwa ne sa’o’i 24 bayan da Majalisar Dinkin Duniya ta ƙara jaddada buƙatar tsagaita wuta cikin gaggawa, inda ta bayyana Gaza a matsayin makabarta ga kananan yara yayin da adadin wadanda suka mutu ya haura 10,000.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp