fidelitybank

Majalisa ta bukaci hukumar Kwastan ta biya diyyar Naira miliyan 390

Date:

Majalisar wakilai ta kasa ta bukaci hukumar kwastan da ta biya diyyar ran mutanen da jami’anta suka kashe da wadanda suka raunata a fadin Najeriya jumullar Naira miliyan 390.

Wannan na cikin shawarar da ke kunshe a rahoton kwamitin majalisar mai kula da harkokin hukumar kwastan, bayan binciken da ‘yan kwamitin suka gudanar kan abin da ya faru a jihar Katsina da kuma jihar Oyo.

Kwamitin ya bayar da shawarar biyan kowane daya daga mutane 10 da ake zargin kwastan sun kashe a Jibia, jihar Katsina ranar 9 ga watan Agusta 2021, a kan diyyar Naira miliyan 20 kowanne daga cikinsu.

Su kuwa mutane 13 da suka samu raunuka a lamarin, a biya su Naira miliyan bibbiyu domin jinya.

Kan rikicin Iseyin a jihar Oyo kuwa, majalisar ta bukaci hukumar kwastan ta biya diyyar mutane hudu da ake zargin jami’anta sun kashe, suma Naira miliyan 20 kowanne, wadanda suka ji rauni kuwa a biya su Naira miliyan biyu kowa.

Majalisar ta nemi a gurfanar da jami’an kwastan din da suke da hannu a kisan ‘yan Najeriya wadanda ba su ji ba ba su gani ba, a gaban shari’a domin a hukunta su ya zama izin ga sauran.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp