fidelitybank

Majalisa ta bukaci hukumar Kwastan ta biya diyyar Naira miliyan 390

Date:

Majalisar wakilai ta kasa ta bukaci hukumar kwastan da ta biya diyyar ran mutanen da jami’anta suka kashe da wadanda suka raunata a fadin Najeriya jumullar Naira miliyan 390.

Wannan na cikin shawarar da ke kunshe a rahoton kwamitin majalisar mai kula da harkokin hukumar kwastan, bayan binciken da ‘yan kwamitin suka gudanar kan abin da ya faru a jihar Katsina da kuma jihar Oyo.

Kwamitin ya bayar da shawarar biyan kowane daya daga mutane 10 da ake zargin kwastan sun kashe a Jibia, jihar Katsina ranar 9 ga watan Agusta 2021, a kan diyyar Naira miliyan 20 kowanne daga cikinsu.

Su kuwa mutane 13 da suka samu raunuka a lamarin, a biya su Naira miliyan bibbiyu domin jinya.

Kan rikicin Iseyin a jihar Oyo kuwa, majalisar ta bukaci hukumar kwastan ta biya diyyar mutane hudu da ake zargin jami’anta sun kashe, suma Naira miliyan 20 kowanne, wadanda suka ji rauni kuwa a biya su Naira miliyan biyu kowa.

Majalisar ta nemi a gurfanar da jami’an kwastan din da suke da hannu a kisan ‘yan Najeriya wadanda ba su ji ba ba su gani ba, a gaban shari’a domin a hukunta su ya zama izin ga sauran.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp