fidelitybank

Majalisa ta bukaci gwamnati ta rinka baiwa dalibai masu “first class” aiki kai tsaye

Date:

Majalisar wakilai ta bukaci ma’aikatu da sassa da hukumomi da su baiwa ‘yan Najeriya da suka kammala karatun digiri da sakamakon mafi kyau na first class a cibiyoyin Najeriya aiki kai tsaye.

An cimma matsayar ne a ranar Laraba bayan amincewa da kudirin da Chinedu Martins ya gabatar.

A cikin yunƙurin, Martins ya ce, akwai ɗaruruwan ɗalibai masu sakamako na first class na ta gararanba a kan titi ba tare da aikin yi ba.

Ya lura cewa, ɗaliban suna samun nasarar ta hanyar “ƙoƙari mafi girma, aiki mai juriya, ƙuduri, da sanya damuwa.”

Ya jaddada cewa, akwai alaka tsakanin rashin ci gaban Najeriya da kuma yadda ake gujewa wadanda suka kammala digiri da sakamako mafi kyau

“Rashin kasawar Najeriya barin matsayin “kasa mai tasowa”, mai yiwuwa ba zai rasa nasaba da rashin hankali da rashin kishin siyasa na masu mulki da masu tsara manufofin bullo da tsarin bayar da lada ta hanyar da mafi kyawun kwakwalwa za su mamaye muhimman mukamai kai tsaye a cewarsa, zuwa yankin iyawar su,” in ji Martins.

Mataimakin kakakin majalisar, Idris Wase ya nuna adawa da kudirin a kan cewa ya kamata a karfafa wa daliban da suka kammala karatun digiri na daya kwarin guiwa su dauki manyan ayyuka a duniya.

Ya bayyana cewa hukumomi da yawa suna da mafi ƙarancin ƙa’idodin da suke amfani da su wajen tantance aiki ga manyan MDAs.

Shugaban majalisar, Femi Gbajabiamila, a lokacin da yake mayar da martani kan kalaman mataimakinsa, ya ce, hukumomi da dama na daukar ma’aikata masu sakamako na 3 wato third class aiki, yayin da masu sakamako na first class ke yawo a kan tituna.

Bayan doguwar muhawara, majalisar ta amince da kudurin.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp