Majalisar wakilai ta bukaci ma’aikatu da sassa da hukumomi da su baiwa ‘yan Najeriya da suka kammala karatun digiri da sakamakon mafi kyau na first class a cibiyoyin Najeriya aiki kai tsaye.
An cimma matsayar ne a ranar Laraba bayan amincewa da kudirin da Chinedu Martins ya gabatar.
A cikin yunƙurin, Martins ya ce, akwai ɗaruruwan ɗalibai masu sakamako na first class na ta gararanba a kan titi ba tare da aikin yi ba.
Ya lura cewa, ɗaliban suna samun nasarar ta hanyar “ƙoƙari mafi girma, aiki mai juriya, ƙuduri, da sanya damuwa.”
Ya jaddada cewa, akwai alaka tsakanin rashin ci gaban Najeriya da kuma yadda ake gujewa wadanda suka kammala digiri da sakamako mafi kyau
“Rashin kasawar Najeriya barin matsayin “kasa mai tasowa”, mai yiwuwa ba zai rasa nasaba da rashin hankali da rashin kishin siyasa na masu mulki da masu tsara manufofin bullo da tsarin bayar da lada ta hanyar da mafi kyawun kwakwalwa za su mamaye muhimman mukamai kai tsaye a cewarsa, zuwa yankin iyawar su,” in ji Martins.
Mataimakin kakakin majalisar, Idris Wase ya nuna adawa da kudirin a kan cewa ya kamata a karfafa wa daliban da suka kammala karatun digiri na daya kwarin guiwa su dauki manyan ayyuka a duniya.
Ya bayyana cewa hukumomi da yawa suna da mafi ƙarancin ƙa’idodin da suke amfani da su wajen tantance aiki ga manyan MDAs.
Shugaban majalisar, Femi Gbajabiamila, a lokacin da yake mayar da martani kan kalaman mataimakinsa, ya ce, hukumomi da dama na daukar ma’aikata masu sakamako na 3 wato third class aiki, yayin da masu sakamako na first class ke yawo a kan tituna.
Bayan doguwar muhawara, majalisar ta amince da kudurin.