Majalisar Dattijai ya umarci Babban Bankin Ƙasa ya sake nazari kan manufofinsa na kuɗi saboda waɗanda ya yi amfani da su a shekara mai bankwana, ba su yi tasiri ba.
Kwamitin kula da bankuna da cibiyoyin kuɗi da na inshora na Majalisar ya kuma nemi jin bahasi a kan matsalar ƙarancin takardun kuɗi da ake fama da ita yanzu, da kuma ƙaruwar tsofaffin kuɗi a hannun mutane.
Matakin na zuwa ne bayan gayyatar da kwamitin ya yi wa Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Olayemi Cardoso don yi musu ƙarin bayani kan nasarorin da bankin ya samu game da manufofinsa na kuɗi a 2024.