fidelitybank

Majalisa ta amince da kudurin dokar karin albashi ga alkalai

Date:

Majalisar wakilai ta amince da ƙudirin dokar neman ƙarin albashi da alawus-alawus ga alƙalan kasar nan.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa wa Majalisar kudirin dokar domin tantancewa tare da amincewa da shi a ranar Talata.

Ƙudirin da aka amince da shi ya bayar da albashin jimlar naira miliyan 5.3 a kowane wata ga alƙalin alƙalai na Najeriya (CJN).

Ƙudirin ya kuma ce sauran alkalan Kotun Koli za su samu albashin naira 4.2 yayin da Shugaban Kotun ɗaukaka ƙara zai rika samun albashin naira miliyan 4.4 duk wata.

Haka kuma, alƙalan kotun ɗaukaka ƙara za su rika karɓar albashin naira miliyan 3.7 duk wata, yayin da ƙaramin alƙali zai karɓi albashin naira miliyan 3.5 duk wata.

A cewar ƙudirin, albashin na wata-wata ya kunshi cikakken albashinsu ne da duk wani alawus-alawus na yau da kullum da suka haɗa da samar da mai da kuma kula da ababen hawa da dai sauransu.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp