fidelitybank

Majalisa ta amince da kudirin neman kafa sabbin makarantun ‘yan sanda

Date:

Majalisar dattawa ta amince da wani kudirin doka da ke neman kafa sabbin makarantun horar da ƴan sanda a kasar nan.

Amincewa da kudirin ya biyo bayan karbar rahoton kwamitin harkokin yan sanda a zaman majalisar na ranar Laraba.

Shugaban kwamitin, Sanata Abdulhamid Ahmed daga jihar Jigawa ne ya gabatar da rahoton.

Yayin gabatar da rahoton, Ahmed ya ce amincewa da kudirin zai taimaka wajen inganta ayyukan cibiyoyin horarwa kuma a ƙarshe ya ƙara wa jami’an ƴan sanda ƙwarewa don samun kyakkyawan sakamako.

Ya bayyana cewa, kudirin idan aka amince da shi, zai ƙara ƙarfafa jami’an ƴan sanda don aiwatar da nauyin da kundin tsarin mulki ya dora musu.

Da yake tsokaci kan kudurin Sanata Abdul Ningi daga Bauchi ya ce yana da muhimmanci a amince da kudirin, domin zai tallafa wa ƴan sanda wajen ayyukansu kuma ya tabbatar da dorewar su.

Ningi ya jaddada muhimmancin samun ƙwararrun ma’aikata don shugabantar hukumar, yana mai cewa amincewa da kudirin zai samar da horon da ake buƙata ga jami’an hukumar.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp