fidelitybank

Majalisa ta amince da kudirin neman kafa sabbin makarantun ‘yan sanda

Date:

Majalisar dattawa ta amince da wani kudirin doka da ke neman kafa sabbin makarantun horar da ƴan sanda a kasar nan.

Amincewa da kudirin ya biyo bayan karbar rahoton kwamitin harkokin yan sanda a zaman majalisar na ranar Laraba.

Shugaban kwamitin, Sanata Abdulhamid Ahmed daga jihar Jigawa ne ya gabatar da rahoton.

Yayin gabatar da rahoton, Ahmed ya ce amincewa da kudirin zai taimaka wajen inganta ayyukan cibiyoyin horarwa kuma a ƙarshe ya ƙara wa jami’an ƴan sanda ƙwarewa don samun kyakkyawan sakamako.

Ya bayyana cewa, kudirin idan aka amince da shi, zai ƙara ƙarfafa jami’an ƴan sanda don aiwatar da nauyin da kundin tsarin mulki ya dora musu.

Da yake tsokaci kan kudurin Sanata Abdul Ningi daga Bauchi ya ce yana da muhimmanci a amince da kudirin, domin zai tallafa wa ƴan sanda wajen ayyukansu kuma ya tabbatar da dorewar su.

Ningi ya jaddada muhimmancin samun ƙwararrun ma’aikata don shugabantar hukumar, yana mai cewa amincewa da kudirin zai samar da horon da ake buƙata ga jami’an hukumar.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp