fidelitybank

Majalisa ta amince da fasalin sauya Naira

Date:

Majalisar dattawa ta amince da ƙudurin babban bankin ƙasar nan na sake fasalin wasu takardun kuɗin ƙasar.

Majalisar ta amince da ƙudurin bayan zazzafar muhawara kan ƙudurin da Sanata Uba sani ya gabatar a zauren kan ƙudurin babban bankin na sake fasalin wasu takardun kudin ƙasar.

Mafiya wayan ‘yan majalisar sun amince da ƙudurin, to sai dai wasu daga ciki sun bayyana damuwarsu game da ranar da babban bankin ya saka na daina karɓar tsoffin kuɗin a faɗin bankunan ƙasar.

Sannan kuma sun ɗiga ayar tambaya kan da alfanun yin hakan game da tattalin arziki, da yadda yin hakan zai sauƙaƙa hauhawar farashin kayyaki da farfaɗo da darajar naira.

Suna masu buƙatar gwamnan babban bankin Godwin Emefiele da ya yi musu ƙarin haske kan waɗannan batutuwa.

‘Yan majalisun sun kuma ce suna fargaba game da illar da hakan za ta haifar ga mazauna karkara da wauraren da ba su da bankuna.

A sanarwar da babban bankin ya fitar game da sake fasalin kuɗin ya ce sabbin kuɗin za su fara yawo daga ranar 15 ga watan Disamban 2022, a yayin da za a daina karɓar tsoffin kuɗin ranar 31 ga watan Janairun 2023.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...
X whatsapp