fidelitybank

Majalisa ta amince a gudanar da ma’aikatar raya yankunan kasar nan da wani kaso na kuɗin jihohi

Date:

Majalisar dattawaa ta amince a riƙa cire kashi 15 na kuɗaɗen gudanar da ma’aikatar raya yankunan ƙasar daga asusun jihohin ƙasar.

A ranar Alhamis ne Majalisar ta amince da ƙudirin bayan la’akari da rahoton kwamitin majalisar kan ayyuka na musamman, wanda shugaban kwamitin Sanata kaka Shehu ya gabatar.

Wannan batu dai ya haifar da zazzafar muhawara a zauren majalisar, inda wasu ‘yan majalisar suka nuna adawa da matakin.

Sanata Yahaya Abdullahi, daga jihar Kebbi ya ce matakin zai sa gwamnatocin jihohi su yi ta shigar da gwamnatin tarayya ƙara, saboda a cewarsa babu jihar da za ta so a riƙa yanke mata kuɗi da nufin ɗaukar nauyin wata ma’aikata ta tarayya.

To sai dai mataimakin shugaban majalisar, Sanata Barau Jibrin daga jihar Kano ya kore fargabar takwaran nasa.

Yana mai cewa ba wai yanke kuɗaɗen jihohin za a yi ba, a maimakon haka kashi 15 cikin 100 na gudanar da ma’aikatar jihohin za su bayar, yayin da gwamnatin tarayya za ta bayar da ragowar.

A ranar Laraba ne shugaban ƙasar Bola Tinubu ya sanar da kafa sabuwar ma’aikata da za ta kula da sauran hukumomin raya yankuna, bayan rushe ma’aikatar raya yankin Naija Delta.

A yanzu ƙasar na da hukumomin raya yankuna da suka haɗa da ta yankin Naija Delta da ta arewa maso gabas da ta arewa maso yamma, da kuma ta kudu maso gabas.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp