fidelitybank

Majalisa na sane da halin da ƴan Najeriya ke ciki – Tajudeen Abbas

Date:

Kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, ya ce, majalisar na sane da halin matsalar tsaro da tsadar rayuwa da ‘yan ƙasar ke fuskanta.

Honarabul Tajudeen Abbas ya ce a ɓangarensu na majalisa ba za su zuba wa ɓangaren zartaswa ido ba har sai an samu mafita.

Kakakin majalisar ya tabbatar wa da BBC cewa za a shawo kan ƙalubalen da ake fuskanta nan ba daɗewa ba.

”Majalisa za ta yi duk abin da ya kamata domin ganin an samu sauƙi a matsalar tsaro da tsadar rayuwa da ke fuskanta a ƙasar nan”.

Kakakin majalisar ya ce majalisa ta za kirawo duka masu ruwa da tsaki a harkar tsaro domin magance matsalar tsaron da ake ciki.

Honarabul Tajedeen Abbas ya ce ‘yan majalisar na sane da irin halin matsin rayuwa da talakawan ƙasar ke ciki, kuma suna duk mai yiwuwa domin magance matsalar.

Don haka ne ma ya ce ‘yan majalisar suka mayar da hankali wajen sayen kayan abinci domin rabar wa talakwan da suka zaɓe su.

Ya kuma ce gwamnati na yin duk mai yiwuwa don magance matsalar, kuma ya tababtar da cewa nan ba da jimawa ba farashin kayan abincin zai sauka a ƙasar.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp