fidelitybank

Majalisa ku yi watsi da kudirin lura da shafukan sada zumunta a Najeriya – SERAP

Date:

Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci da tabbatar da dimokradiyya a Najeriya, ta buƙaci shugabannin majalisun dokokin biyu, su yi watsi da kudirin lura da shafukan sada zumunta a

ƙasar.

Cikin wata sanarwar da ƙungiyar ta fitar , a ce kudurin idan ya zaman doka, zai taƙaita ‘yancin faɗar albarkacin baki da ɓoye sirri.

SERAP ta buƙaci gwamnatin ƙasar ƙarƙashin jagorancin shugaba Tinubu ta daina yunƙurin tilasta wa manyan kamfanonin fasaha na Google da Youtube taƙaita wannan ‘yanci na ɗan’adam.

Rahotonni sun ambato babban mataimakin daraktan ƙungiyar, Kolawole Oluwadare, na cewa ƙudurin zai mayar da ”halastaccen ‘yancin ɗan’adam zuwa laifi”

Ya ƙara da cewa “duk wani yunƙuri na sanya idanu domin lura da shafukan sada zumunta, za mu ɗauke shi a matsayin abin da ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya da dokokin ‘yancin ɗan’adam na ƙasa-da-ƙasa.”

An dai daɗe ana ta kiraye-kiraye ga hukumomin ƙasar da su yi wata doka da za ta riƙa lura da abubuwan da ake wallafawa a shafukan sada zumunta, sakamakon yawaitar yaduwar labaran ƙarya da na cin zarafi a shafukan.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp