fidelitybank

Majalisa dokokin Kano ta amince da gyaran dokar majalisar masarautu

Date:

Majalisar dokokin jihar Kano, ta amince da gyaran dokar majalisar masarautun jihar ta shekarar 2019 a zamanta na yau Talata a zamanta wanda shugaban majalisar Rt Hon Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari ya jagoranta.

An zartar da kudurin dokar ne bayan da aka gudanar da zaman tattaunawa a cikin kwamitin baki daya na majalisar.

Hakazalika, a zaman na yau, majalisar ta samu takarda daga Gwamnan Zartarwa na neman a tantance tare da tabbatar da nadin Barista Mahmoud Balarabe a matsayin babban shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano. Majalisar ta mika wasikar ga zaunannen kwamitin majalisar kan yaki da cin hanci da rashawa domin ci gaba da gudanar da ayyukan majalisar.

Hakazalika, majalisar ta kuma samu wasika daga Gwamnan Zartaswa kan daftarin kudirin kafa hukumar kula da hanyoyin karkara, kuma wasikar ta mika wa majalisar, domin daukar mataki. Gwamnan ya kuma aike da wata wasika kan wakar jihar Kano da gwamnatin jihar Kano da jami’ar Bayero suka kirkira domin tantancewa tare da kafa doka da kuma na daftarin dokar ba da izinin mallakar filaye da tsare-tsare na 2022 (1443 A.H.) domin tattaunawa tare da zartar da doka ta Majalisa.

Majalisar ta kuma samu takardar neman a tabbatar da Balarabe Hassan Karaye a matsayin cikakken kwamishina a hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano da na hukumar bayar da gudunmawar lafiya ta jihar Kano gyara mai lamba biyu na shekarar 2922 (1444 A.H.).

An ba da wasiƙun ga kwamitocin da suka dace don ƙarin ayyukan majalisa.

Majalisar ta dage zamanta zuwa gobe Laraba, a wani kudiri da shugaban masu rinjaye kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Warawa, Hon. Labaran Abdul Madari, kuma Hon. Sale Ahmed Marke, Memba mai wakiltar mazabar Dawakin Tofa.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp