fidelitybank

Mainz ta soke kwantiragin ɗan wasan ta Eli Ghazi bayan ya goyi bayan Falasɗinu

Date:

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Mainz ta soke kwantiragin Anwar El Ghazi ɗan ƙasar Holland saboda wani sakon da ya wallafa a dandalin sada zumunta na goyon bayan Falasɗinawa a rikicin Isra’ila da Gaza, kamar yadda kulob ɗin ya tabbatar a ranar Juma’a.

Kulob ɗin na Bundesliga ya dakatar da ɗan wasan mai shekaru 28 a ranar 17 ga watan Oktoba bayan wani saƙon da yanzu ya goge a shafukan sada zumunta wanda ya nuna goyon bayan Falasdinawa.

A ranar Litinin, Mainz ta ɗage dakatarwar da aka yi masa tare da yi masa gargaɗi a hukumance.

Amma a ranar Juma’a, ƙungiyar ta sanar da cewa ta soke kwantiragin El Ghazi ”nan take”.

“FSV Mainz 05 tana kawo ƙarshen dangantakarta da Anwar El Ghazi kuma ta sallami ɗan wasan a ranar Juma’a. Ƙungiyar ta ɗauki wannan matakin ne a matsayin martani ga kalamai da rubuce-rubucen ɗan wasan a shafukan sada zumunta,” in ji Mainz.

A baya Mainz ta ce sakon El Ghazi ya ɗauki ”matsaya kan rikicin Gabas ta Tsakiya da ba ta daidaita da matsayar kulob ɗin ba.”

El Ghazi ya ƙulla yarjejeniya da Mainz a bazaran da ta wuce kuma ya buga wasanni uku a kakar wasa ta bana

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp