Jamiāan hukumar tsaro ta Yamma, Amotekun Osun Corps, sun cafke wani mutum mai suna Yisa Aderibigbe da laifin yiwa wasu kananan yara biyu fyade a Osogbo, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar da Birgediya Janar Bashir Adewinmbi, Kwamandan rundunar Osun Amotekun, Aderibigbe ya bayyana a ranar Alhamis din da ta gabata bayan wani rahoto da mazauna yankin suka yi masa inda ya aikata wannan danyen aiki.
An tattaro cewa Yisa ya kwashi kananan yara biyu masu shekaru 5 da 7 a wani gini da ba a kammala ba a unguwar Ayepe da ke Osogbo tare da yi musu fyade.
Adewinmbi ya kuma bayyana cewa bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya shahara kuma mai yawan fyade.
āDa aka yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa laifin aikata laifin.
āIna so in gode wa mazauna yankin, wadanda suka sanar da mu lamarin. Ina so in yaba musu bisa goyon bayan da suke bayarwa,ā in ji shi a cikin sanarwar.
Ya ce an mika wanda ake zargin ga āyan sanda domin yi masa tambayoyi da kuma gurfanar da shi gaban kuliya.
A yayin da yake jaddada kudirin rundunar na yaki da miyagun ayyuka a jihar, ya ce Amotekun zai yi aiki tare da sauran jamiāan tsaro a kodayaushe domin kawar da masu aikata laifuka a jihar.
Kwamandan rundunar, wanda ya yi gargadin cewa ba daidai ba ne a siyasantar da muggan laifuka, ya kara da cewa dole ne a maida hankali wajen tabbatar da tsaron jamaāa, tare da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro.