fidelitybank

Mai tsaron raga da mai horaswa a Algeria sun mutu bayan mumunan hatsari

Date:

Wani haɗarin mota da ya faru a Algeria ya halaka ɗan wasa da kocin ƙungiyar ƙwallon kafa ta Mouloudia Club El Bayadh lamarin da ya tilastawa hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar ɗage dukkan wasannin da aka tsara bugawa.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasar ya ce mai tsaron ragar ƙungiyar Zakaria Bouziani mai shekara 27 da mataimakin koci, Khalid Muftah sun mutu sanadin haɗarin.

Ƴan wasan na hanyar zuwa Tizi Ouzou domin buga wasa da JS Kabylie ranar Juma’a lokacin da motar ɗauke da tawagar ƴan wasan ta yi haɗari kusa da birnin Tiaret da ke arewa maso yammacin Algeria, a cewar kafafen yaɗa labaran ƙasar.

Shugaban Algeria, Abdelmajid Tebboune ta ce cikin wata sanarwa cewa ya samu rahoton ibtila’in tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan ƴan wasan da suka rasa ransu.

Ƙungiyar a saƙon da ta wallafa a shafukan sada zumunta ta ce sauran ƴan wasan da suka ji rauni ba sa cikin wani mummunan yanayi.

A cewar sanarwar, hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar ta yanke shawarar dakatar da duk wasannin da aka shirya yi a ƙarshen mako

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp