fidelitybank

Mai shekaru 42 ya rataye kansa a kan bishiya a Jigawa

Date:

Wani mutum dan shekara 42 mai suna Ibrahim Adamu Mohd ya kashe kansa ta hanyar rataya a kan bishiya a unguwar Kanti da ke karamar hukumar Kazaure a jihar Jigawa.

Wani mazaunin garin ya shaidawa DAILY POST cewa lamarin ya faru ne a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da mazauna garin Kanti suka tashi da safe, suka tarar da wani mutum da ba a san ko wanene ba, da igiya a wuyansa, yana rataye a jikin bishiya.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar wa DAILY POST faruwar lamarin.

Ya ce wanda aka kashe din mai suna Ibrahim Adamu dan asalin kauyen Gayawa ne da ke karamar hukumar Ungogo ta jihar Kano.

Ya ce, Mista Ibrahim ya kashe kansa ne ta hanyar rataya a kan titin Daura Road Adjacent Baushe a garin Kazaure a wani gini da bai kammala ba.

Shiisu ya ce an samu katin gayyata da katin SIM guda biyu a hannunsa.

Ya ce ana ci gaba da bincike don gano musabbabin mutuwarsa.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp