fidelitybank

Mai shekaru 42 ya rataye kansa a kan bishiya a Jigawa

Date:

Wani mutum dan shekara 42 mai suna Ibrahim Adamu Mohd ya kashe kansa ta hanyar rataya a kan bishiya a unguwar Kanti da ke karamar hukumar Kazaure a jihar Jigawa.

Wani mazaunin garin ya shaidawa DAILY POST cewa lamarin ya faru ne a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da mazauna garin Kanti suka tashi da safe, suka tarar da wani mutum da ba a san ko wanene ba, da igiya a wuyansa, yana rataye a jikin bishiya.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar wa DAILY POST faruwar lamarin.

Ya ce wanda aka kashe din mai suna Ibrahim Adamu dan asalin kauyen Gayawa ne da ke karamar hukumar Ungogo ta jihar Kano.

Ya ce, Mista Ibrahim ya kashe kansa ne ta hanyar rataya a kan titin Daura Road Adjacent Baushe a garin Kazaure a wani gini da bai kammala ba.

Shiisu ya ce an samu katin gayyata da katin SIM guda biyu a hannunsa.

Ya ce ana ci gaba da bincike don gano musabbabin mutuwarsa.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon É—an takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...

Jihohin Najeriya tara da za a iya samun ambaliya ciki harda Kano

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya Nimet, ta yi hasashen...

Tsohon sakataren gwamnatin a mulkin Buhari ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, SGF, Babachir Lawal ya fice...

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faÉ—a wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaÆ™i da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunÆ™asa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...
X whatsapp