fidelitybank

Amaryar da ta raba jarkar fetur a matsayin tagomashin biki ta yi nadama

Date:

Pearl Ogbolu, ‘yar asalin Legas wacce aka fi sani da Erelu Okin, ta nemi afuwar ta na raba man fetur a matsayin abin tunawa a bikinta.

A ‘yan makonnin da suka gabata ‘yan Najeriya na fama da matsalar karancin man fetur, bayan da aka samu matsala a harkar samar da man fetur.

Kwanan nan wani faifan bidiyo ya yaɗu a shafukan sada zumunta wanda ke nuna ana rarraba man fetur a matsayin abin tunawa a taron Ogbolu na Legas.

Shagalin bikin wanda aka gudanar a ranar 4 ga Maris, ya jawo cece-ku-ce daga ‘yan Najeriya. A kuma ranar Asabar din da ta gabata ne gwamnatin jihar Legas ta rufe Havilah Event Centre, inda aka gudanar da bikin, bisa laifin saba ka’idojin kare lafiyar jama’a.

Daga bisani, Abiodun Alabi, kwamishinan ‘yan sandan Legas, ya bayar da umarnin kamo wadanda ke da hannu wajen rabon kayayyakin ajiyar man fetur.

Adekunle Ajisebutu, mai magana da yawun ‘yan sandan Legas, ya sanar da ci gaban, inda ya bayyana abin da Ogbolu ta yi a matsayin “abin zargi”.


A wani sako da ta wallafa a shafinta na Instagram, Ogbolu ta ce: “Ina so in yi amfani da wannan kafar, domin neman afuwa kan yadda aka shigo da kayayyakin ajiyar man fetur cikin zauren bikin.

“Niyyata ita ce, kawai in nuna godiya ga baƙi na domin halartar taron na a cikin waɗannan lokutan wahala.

“Na dakata domin yin tunani da kuma ba da hakuri da gaske, kuma na gode muku duka, saboda fahimtar ku da sukar ku.” A cewar ta.

Tun da farko kwamishinan yada labarai Gbenga Omotosho ya ce jihar za ta binciki lamarin.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp