Wani ma’aikaci mai haƙan rijiya mai suna Abba Yusuf, dan shekara 25, ya tsallake rijiya da baya, a Kano ranar Talata, saboda gaggawar ceto da hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta yi masa.
Yusuf yana hakar rijiya a unguwar Hotoron Mahauta da ke Kano, sai ya fada ciki ta binne shi cikin rairayi.
“Mutumin ya makale ne a lokacin da yake tona rijiyar a lokacin zafi kuma rashin iska ya sa ya kusa mutuwa,” in ji Alhaji Saminu Abdullahi, kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano.
“Mun samu kiran gaggawa daga wani Abubakar Haruna, kuma nan take muka aika da tawagarmu zuwa wurin da abin ya faru.
“An ceto Yusuf da ransa kuma aka kai shi Asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano, domin yi masa magani.
Abdullahi ya kara da cewa, “Daga baya an mika shi ga wani sufeto na ‘yan sanda a ofishin ‘yan sanda na Kofar Wambai.