fidelitybank

Mahara sun kashe tsohon Soja da mutane 15 a Benue

Date:

Wasu da ake zargin makiyaya ne dauke da makamai a yammacin ranar Alhamis, sun kai hari Wandor, a unguwar Mbaikyor da ke gundumar Mbalom a karamar hukumar Gwer ta Gabas, a karamar hukumar Gwer ta jihar Benue, inda suka kashe wani jami’in soja mai ritaya, da wasu 15.

Maharan sun kuma kone gidaje sama da 50 da bukkoki da filayen gonaki da rumbunan abinci a matsugunai 11 a harin.

Jaridar DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, harin ya afku ne kimanin shekaru shida bayan wani harin makamancin haka da wasu makiyaya dauke da makamai suka kai a cocin St. Ignatius Catholic Church, Ukpor Parish, karamar hukumar Mbalom Gwer ta Gabas, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu limaman cocin Katolika guda biyu da wasu mabiya coci 17.

Wani da ya tsira daga harin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ā€˜yan fashin dauke da muggan makamai wadanda yawansu ya kai kimanin 40 ne suka abkawa al’ummar da misalin karfe 7 na dare inda suka bude wuta kan mutanen yankin da ba a sani ba.

Shugabar riko ta karamar hukumar Gwer ta Gabas, Misis Comfort Agbo, yayin da take tabbatar da faruwar lamarin ta ce, ā€œa halin yanzu akwai zaman lafiya a yankin na Wandor. Ya zuwa yanzu an gano gawarwaki 16. Biyu sun jikkata kuma suna karbar magani.

ā€œWadanda suka kai hari tare da kashe mutanena ana zargin makiyaya ne da makamai. Yanzu haka dai jami’an tsaro na kwashe gawarwakin zuwa dakin ajiyar gawa.ā€

Jami’in hulda da jama’a na ā€˜yan sandan, Sufeto, SP, Catherine Anene, wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce kwamishinan ā€˜yan sandan na kan hanyarsa ta zuwa inda aka kai harin domin tantancewa.

A halin da ake ciki, mataimakin gwamnan jihar, Sam Ode, an ce shi ma ya jagoranci tawagar zuwa al’umma.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp