Rahotanni sun ce an kashe aƙalla mutum 14, sannan an jikkata wani a wani hari da aka kai a garin Gidan Ado da ke ƙaramar hukumar Riyom da ke jihar Filato.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito daga sakataren watsa labaran ƙungiyar ci gaban mutanen Irigwe wato Irigwe Community Development Association (IDA) Sam Jugo cewa an kashe musu mutum 14, sannan ya ce daga baya sun sanar da dakarun operation safe haven, inda suka kawo musu ɗauki.
Sai dai kakakin dakarun wanzar da zaman lafiya na jihar bai amsa kiran waya ba, haka shi ma kakakin rundunar ƴansandan jihar.
Ƙungiyar ta ce an kai harin ne kwana biyu bayan rundunar ƴansandan jihar ta tura jami’anta domin tabbatar da an gudanar da shagulgulan Kirsimeti da Sabuwar Shekara cikin lumana.