Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wani mahajjaci Sani Idris-Muhammed a kasar Saudiyya yayin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2022.
Sakataren zartarwa na hukumar jin dadin alhazai ta jiha, Alhaji Muhammed Abba-Danbatta ne ya bayyana hakan ga manema labarai a ranar Asabar.
Ya ce, Idris-Muhammed wanda ya fito daga karamar hukumar Madobi, ya rasu ne a ranar Asabar bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a babban asibitin Makkah.
A cewarsa, an yi jana’izar marigayin kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a babban masallacin Juma’a da ke farfajiyar Masallacin Harami na Shira a Makkah.
Abba-Danbatta ya yi wa marigayin addu’a tare da ta’aziyya tare da iyalansa.