Saudiyya ta tarbi rukunin farko na alhazai daga wata kasa tun bayan barkewar cutar korona a watan Maris na 2020.
Kafofin yada labaran Saudiyya sun ce an tarbi mahajjata 358 daga kasar Indonesia da dabino da faranni.
A shekaru biyu da suka gabata an rage yawan maniyyatan da za su shiga birnin Makkah, amma a Yulin bana Musulmi daga sassan duniya za su yi aikin Hajji (Daya daga cikin shika-shikan Musulunci guda biyar.
Hajji wajibi ne ga duk musulmin da yake da hali akalla sau daya a rayuwarsa.