fidelitybank

Mahaifina ya tilasta min auren dole – Matashiya

Date:

Wata mata mai suna Fatima ta kai mahaifinta gaban kotun shari’a da ke zamanta a jihar Kaduna, saboda mahaifinta ya tilasta mata auren dole.

Fatima mai shekaru 20 ta shaida wa kotun cewa, tana da wanda take so amma mahaifinta, Aliyu Muhammad ya yi barazanar kai ta kauye ya aurar da ita.

Lauyan Fatima, Malam Bulama ya kuma shaida wa kotun cewa wanda yake karewa bai shigar da kara a kan mahaifinta ba saboda rashin girmama shi.

Bulama ya ce: “Uban yana son wanda nake karewa ya auri wani mutum a kauyensu da ke jihar Neja. A yanzu haka tana zaune a gidan auntynta domin ya yi mata barazanar zai kai ta kauye ya aure ta.

Shi ma a nasa bangaren, mahaifin Fatima, Aliyu Muhammad ya ce iyayensa da suka rasu sun zabi mijin ga diyarsa kafin rasuwarsu kuma ya mutunta bukatunsu.

“Na aurar da ‘ya’yana mata 6 a kauyen kuma suna nan lafiya. Mahaifiyar Fatima ita ce kwakwalwar da ke bayan taurin kanta. Ina bukatan izini domin in tuntubi jama’ata kan wannan al’amari,” inji shi.

Alkalin kotun, Isiyaku Abdulrahman, ya ce uba a karkashin dokar Shari’a, yana da hakkin ya zabar wa diyarsa mijin aure.

Sai dai ya lura cewa ba a karfafa auren dole.

“Kai ne mahaifinta, don haka ka ba ta damar gabatar da wanda take so ta aura, idan kuma kana son addininsa da halayensa ka yarda ta yi aure,” in ji kotun.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp