Shugaban ofishin hukumar jarabawar Afirka ta Yamma a Najeriya (WAEC), Patrick Areghan, a ranar Alhamis, ya ce, an kama wasu ma’aikata kusan 10, bisa zarginsu da hannu wajen tafka magudin jarrabawar kammala sakandare da ake yi.
Areghan, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake duba jarrabawar a cibiyoyi hudu a Abuja, ya ce, an kama su ne a jihohin Legas da Kano da Beyelsa da kuma Kaduna.
“Babban matsalarmu ta ta’allaka ne a kan masu kula da su saboda kadan ne daga cikinsu suke da abin dogaro, kuma abin takaici wadannan su ne masu kula da ma’aikatar ilimi ta jihohi daban-daban ta nada muka dauke su aiki. Ba mu da ikon zaɓe kowane mai kula da kanmu kawai mun yi amfani da ƙwararrun malamai da ma’aikatar ta kawo mana.