Ministan harkokin ‘yan sanda, Mohammed Maigari Dingyadi, ya ce, tsohon mukaddashin shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu zai gurfana a gaban kotu ne kawai idan an kawo rahoton binciken da ake gudanarwa a kan shi da mai shari’a Justice Ayo Salami, ke jagoranta.
Ya bayyana haka ne a jiya ya yin taron ministoci na mako-mako wanda tawagar ‘yada labarai na shugabancin Najeriya a Abuja.
A watan Yulin 2020, shugaba Muhammadu Buhari ya kafa wata tawaga da za ta gudanar da bincike kan zarge-zargen da ake yi wa Magu, biyo bayan koken da Antoni Janar na kasa ya shigar Abubakar Malami. In ji BBC.