Wasu ‘ya’yan jam’iyyar PDP, sun sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a jihar Sokoto.
Shugaban jam’iyyar APC a jihar wanda ya karbi masu sauya shekar a ranar Lahadi, ya ce, sabuwar sauya shekar da suka yi ita ce wasu tarin dimbin ‘ya’yan jam’iyyar PDP daga gundumomin Dundaye, Gumburawa da Gidan Bubu a karamar hukumar Wamakko.
Ministan harkokin ‘yan sanda, Maigari Dingyadi, wanda ya yi jawabi a wajen taron, ya bayyana ci gaban da aka samu a matsayin nasara.
“Gwamnatin APC a karkashin kulawar shugaban kasa Muhammadu Buhari ta kawo ayyukan raya kasa masu inganci da nufin yin tasiri ga rayuwar mutane.”
“Gwamnati ta kwashe shekaru bakwai da rabi tana ci gaba da aiwatar da shirye-shirye masu dorewa wadanda ke tasiri ga rayuwar marasa galihu a kasar nan.
“Saboda haka, na yi kira ga dukkan ku da ku ci gaba da goyon bayan nasarar APC domin jam’iyyar ta ci gaba da samar da ribar dimokuradiyya ga jama’armu,” ya bukaci.
Da yake jawabi a wajen taron, shugaban jam’iyyar APC na jihar Isa Sadiq-Achida, ya bayyana wadanda suka sauya sheka a matsayin ginshikan dimokuradiyya a yankin.
Ya kuma bukaci sabbin ‘ya’yan jam’iyyar da su samu ‘yanci su kuma yi kokarin ganin jam’iyyar ta samu nasara a zabe mai zuwa a jihar.