fidelitybank

Magoya bayan Obi sun yi zanga-zanga a Abuja

Date:

Dubban magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, a ranar Laraba sun gudanar da zanga-zanga a babban birnin tarayya, bisa zargin magudin zaben da aka yi a ranar Asabar.

Masu zanga-zangar wadanda yawancinsu matasa ne, sun yi dandazo ne a Unity Fountain Abuja da safiyar ranar Laraba domin neman a soke sakamakon zaben shugaban kasa da ake zargin an sauya.

Manajan yakin neman zaben jam’iyyar Labour Party, Isaac Balami wanda ya zanta da DAILY POST a wurin zanga-zangar, ya yi zargin cewa wakilan jam’iyyar na da sakamako daban da wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta sanar.

Karanta Wannan: INEC ta baiwa Tinubu da Shettima shaidar lashe zaben su

Ya ce, “Mun zo nan ne domin mu kunna tsarin dawo da wa’adin sata. Mun yi imani kuma muna da tarihi cewa APC ba ta ci zaben nan ba.

“Muna da sakamakonmu. Sakamakon da suka sanar ba shine wakilanmu ba. Ba mu zo muna fada ba, muna nan ne mu shaida wa duniya cewa an sace mana mandat dinmu ba wai kawai za mu zauna a gida mu yi kuka ba”.

Ku tuna cewa Shugaban INEC, Mahmood Yakubu ya bayyana Bola Tinubu na jam’iyyar All Progressives Congress, APC ne ya lashe zaben.

Tinubu ya samu kuri’u 8,794,726 inda ya kayar da abokan hamayyarsa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da Peter Obi na jam’iyyar Labour, LP wanda ya samu kuri’u 6,984, 520 da 6,101,533 bi da bi.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp