fidelitybank

Magoya bayan mu ku daina lalata kadarorin APC – PDP

Date:

Jam’iyyar adawa ta PDP a jihar Zamfara, ta gargadi magoya bayanta da su daina barnata kadarori na jam’iyyar APC.

Sakataren jam’iyyar, Faruk Shettima Rijiya ya ce jam’iyyar PDP ta lashe zaben gwamna a jihar ba ta baiwa kowa ikon lalata kadarori na ‘yan adawa ko na daidaikun mutane ba.

A wata tattaunawa da ya yi a Gusau, ya ce, “Ba ma cikin irin wannan shiri kuma ba za mu taba goyon bayan irin wannan rashin adalci ta kowace fuska ba.

“Jihar Zamfara na bukatar a mayar da matsayinta ba wai a lalata dukiyoyin da ake da su ba, jam’iyyar ta nesanta kanta da duk wanda aka samu yana yin haka.”

Ya ce gwamnati mai zuwa ba ta da niyyar farautar kowa, inda ya ce rade-radin da ake ta yadawa a jihar na cewa Gwamna Bello Mohammed Matawalle ne ake kai wa hari, karya ne.

“Ba mu yiwa kowa hari ba amma duk wanda aka samu da laifin doka dole ne ya fuskanci sakamakon shari’a saboda babu wanda za’a mayar da saniya mai tsarki ko kuma wanda ba za a iya tabawa ba saboda sabuwar gwamnati ta shirya kama su.

“Rushe jam’iyyun adawa ko kadarori na daidaikun jama’a ba ya taimaka wa gwamnati mai zuwa a kowane mataki sai dai a bar magoya bayansu su ci gaba da biyayya ga jam’iyyar.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp