fidelitybank

Magoya bayan Manchester United za su yi zanga-zanga a kan makomar ƙungiyar

Date:

Magoya bayan Manchester United sun shirya wata zanga-zangar nuna adawa ga mamallakan kulob ɗin kafin wasan United da Luton ranar Asabar a yayin da suke buƙatar a sayar da ƙungiyar.

Ƙungiyar magoya bayan United ta dakatar da adawa da dangin Glazer bayan mutuwar Sir Bobby Charlton.

Sai dai suna kira ga magoya bayansu da su hallara a kusurwar arewa maso yammacin filin wasan domin abin da suka bayyana a matsayin zanga-zangar lumana.

Wannan dai za ta kasance zanga-zanga ta farko tun bayan da aka bayyana cewa Sir Jim Ratcliffe na fatan sayen ƙaramin hannun jari a kulob ɗin, a wani mataki da ke nuna cewa dangin Glazer za su ci gaba da kasancewa masu rinjaye.

Bugu da ƙari, ana sa ran Ratcliffe zai sanya kusan fam miliyan 245 na kuɗinsa don yin aikin garambawul a filin wasan.

Majiyoyi da dama daga ciki da wajen United sun shaida wa BBC cewa dole ne a hanzarta gaggawar sauya ikon mallakar ƙungiyar, wanda aka ƙaddamar kusan watanni 12 da suka wuce, saboda rashin tabbas da ake fama da shi ba ya taimaka wa kociyan ƙungiyar Erik ten Hag.

United ta yi rashin nasara a wasa na tara cikin 17 a kakar wasan bana a Copenhagen kuma tana fuskantar yiwuwar ƙasa kai wa zagaye na gaba a gasar zakarun Turai.

Sau huɗu ne kawai suka kai zagaye na biyu a gasar tun bayan da Sir Alex Ferguson ya yi ritaya a shekarar 2013.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp