fidelitybank

Magoya bayan Manchester United za su yi zanga-zanga a kan makomar ƙungiyar

Date:

Magoya bayan Manchester United sun shirya wata zanga-zangar nuna adawa ga mamallakan kulob ɗin kafin wasan United da Luton ranar Asabar a yayin da suke buƙatar a sayar da ƙungiyar.

Ƙungiyar magoya bayan United ta dakatar da adawa da dangin Glazer bayan mutuwar Sir Bobby Charlton.

Sai dai suna kira ga magoya bayansu da su hallara a kusurwar arewa maso yammacin filin wasan domin abin da suka bayyana a matsayin zanga-zangar lumana.

Wannan dai za ta kasance zanga-zanga ta farko tun bayan da aka bayyana cewa Sir Jim Ratcliffe na fatan sayen ƙaramin hannun jari a kulob ɗin, a wani mataki da ke nuna cewa dangin Glazer za su ci gaba da kasancewa masu rinjaye.

Bugu da ƙari, ana sa ran Ratcliffe zai sanya kusan fam miliyan 245 na kuɗinsa don yin aikin garambawul a filin wasan.

Majiyoyi da dama daga ciki da wajen United sun shaida wa BBC cewa dole ne a hanzarta gaggawar sauya ikon mallakar ƙungiyar, wanda aka ƙaddamar kusan watanni 12 da suka wuce, saboda rashin tabbas da ake fama da shi ba ya taimaka wa kociyan ƙungiyar Erik ten Hag.

United ta yi rashin nasara a wasa na tara cikin 17 a kakar wasan bana a Copenhagen kuma tana fuskantar yiwuwar ƙasa kai wa zagaye na gaba a gasar zakarun Turai.

Sau huɗu ne kawai suka kai zagaye na biyu a gasar tun bayan da Sir Alex Ferguson ya yi ritaya a shekarar 2013.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp