Ana ci gaba gudanar da zanga-zanga a biranen duniya don nuna goyon baya ga al’ummar Falasɗinawa musamman na Zirin Gaza.
Yau kwana na 15 ke nan da Isra’ila fara luguden wuta a kan birnin bayan harin da Hamas ta kai mata ranar 7 ga watan Oktoba, inda suka kashe mutum 1,400 kuma akasarinsu farar hula.
Sai dai zuwa yanzu, Isra’ila ta kashe mutum 4,385 a hare-haren ramuwar gayya kan Gaza da kuma sauran garuruwan Falaɗinawa da ta mamaye.

