fidelitybank

Magoya bayan Arsenal na cigaba da yin gunaguni bayan an yi musu bugun Sakwara

Date:

Magoya bayan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal na ci gaba da bayyana ra’ayinsu kan rashin nasara da ƙungiyar ta yi a hannun Newcastle a wasan kusa na da ƙarshe a gasar Carabao.

Ƙungiyar dai ta yi rashin nasara da ci 2-0 da nema a wasan da suka kara a filin wasa na St. James’ Park.

Rashin nasarar da Arsenal ta yi a gidan Newcastle na nufin ta sha kaye da ci 4-0 gida da waje da suka buga a matakin wasan kusa da na ƙarshe na gasar.

Alhaji Yaman mai Arsenal ɗan asalin jihar Kano mazaunin Legas, ya ce wannan wasa bai yi musu ɗaɗi ba.

”Newcastle sun ci mutuncin Arsenal, a gidanmu sun ci mu 2-0, sannan a gidansu sun yi mana 2-0”.

”Wannan abin takaici ne yadda ƙungiyarmu ke kan ganiya a bana, amma a ce ko ƙwallo guda mun kasa ci a duka wasannin biyu, gida da waje”.

Shi kuwa Safiyan Mai Arsenal cewa ya yi wasan bai ba shi mamaki ba, la’akari da cewa tuna wasan farko Newcastle ta ci su 2-0 a wasan farko da aka buga a Emirates.

”Dama na san zai yi wahala mu je gidansu mu yi musu 3-0,” kamar yadda ya ce.

Ƙungiyar – da Mikel Arteta ke jagoranta – yanzu za ta mayar da hankali kan kofin Premier da take fatan lashewa, bayan da take mataki na biyu da tazarar maki shida tsakaninta da Liverpool ta ɗaya.

Haka kuma Gunners ɗin ta kai matakin wasan zagayen ‘yan 16 a gasar Zakarun Turai ta Champions League.

Rabon da Arsenal ta ɗauki wani kofi dai tun 2020 lokacin da ta ɗauki kofin FA Cup.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp