Magoya bayan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal na ci gaba da bayyana ra’ayinsu kan rashin nasara da ƙungiyar ta yi a hannun Newcastle a wasan kusa na da ƙarshe a gasar Carabao.
Ƙungiyar dai ta yi rashin nasara da ci 2-0 da nema a wasan da suka kara a filin wasa na St. James’ Park.
Rashin nasarar da Arsenal ta yi a gidan Newcastle na nufin ta sha kaye da ci 4-0 gida da waje da suka buga a matakin wasan kusa da na ƙarshe na gasar.
Alhaji Yaman mai Arsenal ɗan asalin jihar Kano mazaunin Legas, ya ce wannan wasa bai yi musu ɗaɗi ba.
”Newcastle sun ci mutuncin Arsenal, a gidanmu sun ci mu 2-0, sannan a gidansu sun yi mana 2-0”.
”Wannan abin takaici ne yadda ƙungiyarmu ke kan ganiya a bana, amma a ce ko ƙwallo guda mun kasa ci a duka wasannin biyu, gida da waje”.
Shi kuwa Safiyan Mai Arsenal cewa ya yi wasan bai ba shi mamaki ba, la’akari da cewa tuna wasan farko Newcastle ta ci su 2-0 a wasan farko da aka buga a Emirates.
”Dama na san zai yi wahala mu je gidansu mu yi musu 3-0,” kamar yadda ya ce.
Ƙungiyar – da Mikel Arteta ke jagoranta – yanzu za ta mayar da hankali kan kofin Premier da take fatan lashewa, bayan da take mataki na biyu da tazarar maki shida tsakaninta da Liverpool ta ɗaya.
Haka kuma Gunners ɗin ta kai matakin wasan zagayen ‘yan 16 a gasar Zakarun Turai ta Champions League.
Rabon da Arsenal ta ɗauki wani kofi dai tun 2020 lokacin da ta ɗauki kofin FA Cup.