fidelitybank

Magoya bayan APC sun yi tattalin goyon bayan INEC

Date:

Magoya bayan jam’iyyar All Progressive Congress APC, sun gudanar da wani tattaki a birnin Abuja, wanda suka ce sun yi ne domin nuna goyon baya ga demokuradiyya.

Hakan na zuwa ne kwana guda bayan da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Peopls Democratic Party, PDP, mai hamayya, Atiku Abubakar ya jagoranci zanga-zangar rashin yarda da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Tattakin, wanda magoya bayan jam’iyyar APC ɗin suka shirya, sun ce sun yi ne domin nuna amincewa da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar wanda aka gudanar a watan Fabarairu.

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ayyana Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar, inda zai gaji shugaba mai ci, Muhammadu Buhari, wanda ke kammala wa’adin shugabancinsa na biyu na shekara huɗu-huɗu.

Sai dai manyan jam’iyyun adawa, irin su PDP da LP sun nuna rashin amincewa da sakamakon, inda dukkaninsu suka sha alwashin ƙalubalantar sakamakon a kotu.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp