Jamâiyyar APC reshen jihar Kano, ta yi kira ga mambobinta da magoya bayanta da su kwantar da hankulansu su kasance masu bin doka da oda ko da kuwa sakamakon bukatar da suka yi na sake duba zaben gwamnan jihar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi a ranar 18 ga watan Maris.
Karanta Wannan:Â Magoya bayan APC sun yi zaman dirshen a Abuja har sai an rantsar da Tinubu
Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, inda ya kara da cewa a matsayinsu na masu hannu da shuni sun shahara wajen bin kaâida.
Ya ce, Jamâiyyar za ta yi duk mai yiwuwa a cikin tanade-tanaden doka da sauran tsare-tsare don ganin an tabbatar da adalci a lamarin da kuma amincewa da bukatarsu ta sake duba zaben gwamnan da ya gabata.
Sanarwar ta bayyana cewa, Gwamna Abdullahi Ganduje da mataimakinsa da dan takarar gwamna, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna da mataimakinsa, sun bayyana gamsuwarsu da yadda âyan jamâiyyar suka gudanar da kansu kafin zabe da lokacin da kuma bayan zabe.